✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Za a kwaso ’yan gudun hijirar Sakkwato 50,000 daga Nijar

Akasarin mutanen da za a kwaso ’yan Jihar ta Sakkwato ne

Gwamnatin Tarayya da ta Jihar Sakkwato sun kammala shirye-shiryen kwaso ’yan Jihar kimanin 50,000 da suke gudun hijira a Jamhuriyar Nijar.
Sanata Ibrahim Gobir, dan Majalisar Dattijai mai wakiltar mazabar Sakkwato ta Gabas ne ya sanar da hakan a zantawarsa da maneman labarai a Sakkwato ranar Lahadi.
Ya ce akasarin mutanen da za a kwaso ’yan asalin Kananan Hukumomin Sabon Birni da Isa ne da ke Jihar.
Ya ce, “Na samu tattaunawa da mai ba Shugaban Kasa Shawara Kan Karkokin Tsaro, inda na shaida masa cewa har yanzu mutanen suna can.
“Na fada masa har yanzu suna Jamhuriyar Nijar kuma suna bukatar a dawo da su gida.”
Sanata Gobir ya ce ya akwai bukatar bunkasa harkar tsaro gabanin dawo da mutanen gida.
“Na je har garin Tudun Sunnah kwanan nan, sai da na zubar da hawaye saboda na ga mutane sama da 50,000, ciki har da mata da kananan yara ’yan asalin Jihar Sakkwato,” inji Sanata Gobir.
Ya ce ’yan gudun hijirar na zaune a garuruwan Tudun Sunnah da Shada Kwari da Dadada, dukkansu a Karamar Hukumar Gidan Runji da ke Jamhuriyar Nijar.
Ya ce ya ba su gudunmawar buhu 150 na shinkafa da gero da dawa domin rage musu radadin halin da suke ciki, musamman a watan azumin Ramadan.
Sai dai ya koka cewa har yanzu ana ci gaba da kashe-kashe da satar mutane a yankin Gabashin Jihar.