✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Za a yi Huɗubar Ranar Arfa a harsunan Najeriya 3

Hausa da Fulatanci da Yarbanci na cikin jerin harsunan duniya da gwamnatin Saudiyya ta sanar cewa kai-tsaye za gabatar da fassarar huɗubar Ranar Arfa a…

Hukumomin ƙasar Saudiyya sun sanar cewa a bana za a gabatar wa mahajjata huɗubar Ranar a cikin harsuna uku na Najeriya.

Harsunan Najeriya guda uku da za a gabatar da Huɗubar Ranar Arfa da su sun ne Hausa da Fulatanci da kuma Yarbaci.

Harsunan huda uku na daga cikin  karin harsunan duniya guda 34 da hukumomin Saudiyya suka sanar cewa za a gabatar da Huɗubar a cikinsu.

Ranar Arfa ita ce 9 ga watan Zul Hajji, inda alhazai ke yini a a filin Arfa domin gabatar da ibadoji.

Tsayuwar Arfa ita ce babban rukunin aikin Hajji, wanda sai da shi aikin Hajji ke ciki.

A yayin tsayuwar Arfa, alhazai duka saurari huɗuba, sa’annan su yi sallolin Azahar da La’asar a hade, a matsayin Kasaru, sa’annna su bar filin Arfa kafin faduwar rana su nufi filin Muzdalifa, inda za su kwana, su wayi garin ranar Babbar Sallah a can.