✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

‘’Yan bindigar birni sun karɓe shugabancin Najeriya — El-Rufai

Abin da suka sani kawai shi ne yadda za su karɓi mulki amma ba su san yadda za su yi amfani da shi ba

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya soki tsarin shugabanci na Najeriya na yanzu, inda ya bayyana cewa ‘’yan bindigar birni’ sun karɓe ragamar mulkin ƙasar.

Ya yi wannan jawabi ne a ranar Asabar a Abuja, yayin taron lacca na cika shekaru 60 da haihuwar tsohon Gwamnan Jihar Rivers, Rotimi Amaechi, mai taken ‘Amfani da Talauci a Matsayin Makami a Najeriya.’

El-Rufai ya bayyana cewa a yanzu ne Najeriya take fuskantar matsalolinta mafiya muni tun bayan samar da ita da matsayin ƙasa ɗaya a shekarar 1914.

“Shi ya sa muke tare muna aiki tare da shirya wani haɗin gwiwa don dawo da Najeriya kan turbar da ta dace saboda ta riga ta kauce hanya,” in ji shi.

Ya danganta yanayin da ƙasar ke ciki a yanzu da gazawar shugabanci, inda ya ce, ƙasar “ta kai ga wannan mataki ne saboda mun bar ’yan bindiga, da ke zaune a birane, ba waɗanda ke cikin daji ba, sun karɓe ragamar shugabanci.”

Tsohon gwamnan ya ci gaba da nuna damuwarsa game da abin da ya bayyana a matsayin matsalar rashin ƙwarewa a mulki.

Ya ce, “Ina ganin matsalar da muke da ita, wadda ina ganin Gwamna Babangida ya ambata, ita ce muna samun mutane marasa ƙwarewa mu miƙa musu shugabanci. Yawancinsu ba su san abin da za su yi ba. Abin da sani kawai shi ne yadda za su karɓi mulki amma ba su san yadda za su yi amfani da shi ba,” in ji El-Rufai.

Ya kammala jawabinsa da kira ga ’yan Najeriya da su tashi tsaye su zaɓi shugabannin da ke da cikakkiyar ƙwarewa da ƙarfin hali, da kuma jajircewa don ci gaban ƙasar.