✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Yunwa ce ta haifar da zanga-zangar #EndBadGovernance — PDP

PDP ta ce bai kamata gwamnati ta fake da kama wasu ba, face ita ce silar jefa 'yan Najeriya cikin wahala.

Jam’iyyar adawa ta PDP, ta bayyana cewar tsananin yunwa da ’yan Najeriya ke ciki ne ya haifar da zanga-zangar #EndBadGovernance da aka gudanar a watan da ya gabata.

Daga ranar 1 zuwa 10 ga Agustan 2024, ’yan Najeriya da ƙungiyoyi daban-daban sun fantsama kan tituna domin zanga-zangar nuna rashin jin daɗin yadda matsalolin rayuwa da suka addabi al’umma.

A lokacin wani taron manema labarai da aka gudanar a hedikwatar jam’iyyar a Abuja a ranar Litinin, Sakataren Yaɗa Labaran PDP na ƙasa, Debo Ologunagba, ya bayyana cewa yunwa ce ainihin musabbabin zanga-zangar, ba wasu mutane ba.

Ya buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta mayar da hankali wajen magance yunwa maimakon kama wasu da sunan waɗanda suka ɗauki nauyin zanga-zangar.

Ologunagba, ya bayyana haka ne, bayan kama Shugaban Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya (NLC), Joe Ajearo da DSS ta yi a ranar Litinin.

Ya ce, “Gwamnati tana buƙatar sake dabaru. Mutane sun yi zanga-zanga, maimakon a magance matsalolinsu, sai aka ɓige da kama wasu ana cewa ’yan ta’adda ne, kuma aka ce wasu ne suka ɗauki nauyin zanga-zangar.

“Mun san abin da ya haifar da zanga-zangar—yunwa ce. Gwamnati ta mayar da hankali wajen magance wannan, sai matsalolin su ƙare.

“Manufofin gwamnati masu tsauri suna ƙara jefa mutane cikin wahala. Yanzu za a fara komawa makarantu kuma duk muna ganin irin halin da mutane ke ciki.”