✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Yara 2m ke bukatar agajin jin kai a Nijar —UNICEF

Da farko UNICEF ya yi hasashen miliyan 1.5 ke fama da rashin abinci mai gina jiki, ciki har da akalla 430,000 da ke fama da…

Asusun tallafawa kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana cewa kananan yara sama da miliyan biyu ne ke bukatar agajin jin kai a Jamhuriyar Nijar sakamkon rikicin masu ikirarin jihadi da kuma juyin mulkin baya-bayan a kasar.

Rahoton UNICEF kafin rikicin baya-bayan a Nijar ya kiyasta cewa yara ’yan kasa da shekaru 5 miliyan 1.5 ke fama da rashin abinci mai gina jiki, ciki har da akalla 430,000 da ke fama da tsananin cutar yunwa.

Rahoton UNICEF ya nuna adadin na iya karuwa idan farashin abinci ya ci gaba da hauhawa, da kuma tabarbarewar tattalin arzikin iyalai, da na kudaden shiga.

Bugu da kari, karancin wutar lantarki da tuni ya yawaita a jamhuriyar Nijar da kuma karuwar takunkuman da kungiyar ECOWAS ta kakaba wa kasar, sakamakon juyin mulkin da sojoji suka yi, na iya yin illa ga tasirin alurar rigakafin jarirai da aka adana a cibiyoyin kiwon lafiya.

UNICEF ta bukaci gwamnatin sojin Nijar din da ta bayar da damar shiga kasar ga ma’aikatan jin kai da kayayyaki, kuma ta nemi masu ba da agaji da su kare kudaden jin kai daga takunkumi da kasar ke fuskanta.