✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An janye dokar hana fita a Kaduna da Zariya

Soke dokar hana fita a garuruwan Kaduna da Zariya ta fara aiki nan take

Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna, ya cire dokar hana zirga-zirga da aka kakaba a biranen Kaduna da Zariya.

Kwamishinan tsaron jihar Kaduna, Samuel Aruwan, ya sanar cewa umarnin cire dokar hana fita a Kaduna da Zariya ta fara aiki nan take.

Aruwan ya bayyana cewa majalisar tsaron jihar ta kuma ba da umarnin cewa wajibi ne a samun sahalewar hukumoin da suka dace kafin gudanar da kowane irin taron jama’a a jihar.

A cewar kwamishinan,yin hakan ya zama wajibi ne domin guje wa tashin-tashina ko saba doka da oda.

Gwamna Uba Sani, a cewarsa, ya jinjina wa malaman addini da masru rike da sarautun gargajiya bisa muhimmiyar rawa da suka taka wajen ganin a samu dawowar zaman lafiya a yankunan da aka sanya dokar.