✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan sanda sun kashe ’yan IPOB 5 a Ebonyi

Sai dai jami'an ofishin sun ci karfinsu a wani artabu na tsawon mintuna 30, inda a aka kona motocin ’yan sanda a yayin musayar wuta.

Akalla ’yan kungiyar IPOB biyar aka kashe a wani artabu da ’yan sanda a Jihar Ebonyi ranar Laraba.

’Yan kungiyar a cikin wata motar bas sun kai hari da misalin karfe 9:30 na dare a ofishin ’yan sanda da ke Ishieke a Karamar Hukumar Ebonyi inda suka bude wuta.

Sai dai jami’an ofishin sun ci karfinsu a wani artabu na tsawon mintuna 30, inda a aka kona motocin ’yan sanda a yayin musayar wuta.

Aminiya ta gano cewa jami’ai daga hedikwatar ’yan sandan jihar da sojoji ne suka kai dauki bayan samun kiran gaggawa daga ofishin ’yan sandan na Ishieke.

Wata majiya mai tushe ta ce karar harbe-harben ya tilasta wa mazauna garin guduwa domin tsira da rayukansu.

Majiyar ta ce maharan sun yi kokarin su tsere, amma suka gamu da ajalinsu a hanya a hannun jami’an tsaron.

Rundunar ’yan sandan ba ta fitar da wata sanarwa game da harin ba har zuwa lokacin kammala wannan rahoto.

Amma shaidu sun ce a kai motar da ’yan IPBOB din suka yi amfani da ita da kuma gawarwakinsu hedikwatar ’yan sandan jihar.