✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan sanda sun dakile harin ’yan bindiga kan jami’an INEC

Sun ce ba a samu asarar rai ba a artabun.

’Yan sanda sun dakile wasu ’yan bindiga da ke shirin kai wa jami’an Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) hari a yankin Karamar Hukumar Nnewi ta Kaudu a Jihar Anambra.

Kakakin rundunar ’yan Sandan jihar, DSP Tochukwu Ikenga, ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai (NAN) cewa mazauna yankin ne suka shirya kai harin.

Ikenga ya ce ranar Alhamis da misalin karfe biyar na yamma jami’ansu sun kubutar da wasu jami’an INEC da ke bakin aiki daga cutarwar wasu ’yan bindiga a yankin.

Jami’in ya ce sun yi nasarar dakile harin ba tare da an samu asarar rai ba.

Ya ba da tabbacin jami’ansu su za su ci gaba kokari wajen sauke nauyin da ya rataya a kansu a cikin al’umma.

Daga nan ya yi kira ga al’ummar yankin da su ci gaba da gudanar da harkokinsu ba tare da wata fargaba ba.

(NAN)