✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan sanda sun ceto mutum 97 a dajin Zamfara

Jami'an tsaro sun zagaye dazukan suka fatattaki ’yan bindigar sannan suka ceto mutanen.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Zamfara ta ceto akalla mutum 97 da aka yi garkuwa da su a dajin Shinkafi zuwa Tsafe a jihar.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, CP Ayuba El-Kana ne ya sanar da hakan a taron manema labarai a Gusau ranar Talata.

El-Kana ya ce an yi nasarar ceto mutanen ne sakamakon luguden wutar da jami’an tsaro ke yi a yankunan Shinkafi, Zurmi da Birnin Magaji, wadanda kasurgumin dan bindigar nan Bello Turji ya addaba.

A ranar 3 ga watan Janairu, 2022 ne jami’an tsaro suka samu labarin ganin wasu mutane da ake zargin sace su aka yi a cikin dajin da ke yankin Shinkafi.

A sakamakon haka, hadin gwiwar jami’an tsaro da tubabbun ’yan bindigar yankin da ’yan banga suka shiga dajin, inda suka ceto mutum 68 a dajin.

Kwamishinan ya ce mutanen sun dauki tsawon wata uku a hannun wadanda suka yi garkuwa da su — maza 33, mata 25 ciki har da masu juna biyu, sai kananan yara maza bakwai, mata uku.

Kazalika, El-Kana ya ce a ranar Litinin din ne rundunar ta musamman da aka girke a yankin Tsafe ta shiga dajin Kunchin Kalgo a Karamar Hukumar Tsafe, inda aka ceto mutum 29.

Ya ce mutanen da aka kubutar din sun shafe sama da kwana 60 a hannun ’yan bindigar da suka sace su.

Bayanai sun bayyana cewa kasurgumin dan bindigar nan Ado Aleru ne ya sace mutanen dukkansu tare da tsare su a tsawon lokacin da suka shafe a dazukan.

El-Kana ya ce wadanda aka ceto din suna asibiti inda ake ba su kulawa.

A cewarsa, za a gudanar da bincike sannan a gabatar da su ga gwamnatin jihar, kafin a mika su ga iyalansu.