✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

‘Yan sanda sun ceto mutum 9 da aka sace a Zamfara

Jami'an tsaro sun samu nasarar ceto su bayan wasu bayanai da suka samu.

Rundunar ‘yan sandan Jihar Zamfara ta ceto wasu mutum tara da suka hada da mata bakwai da maza biyu da aka yi garkuwa da su ranar Talata a kauyen Kucheri da ke Karamar Hukumar Tsafe ta jihar.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, CSP Mohammed Shehu Anipr, ya ce an samu nasarar ceto mutanen ne bayan wasu sahihan bayanai da suka samu daga wani basarake.

CSP Shehu, ya ce wadanda ake ceto an kai su asibitin ‘yan sanda da ke Gusau, inda aka duba lafiyarsu kafin daga bisani jami’an tsaro suka sada su da ‘yan uwansu.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Kolo Yusuf ya taya jami’ansa murnar nasarar da suka samu na ceto wadanda lamarin ya rutsa da su.

Ya kuma tabbatar wa jama’a yadda suke ci gaba da kai hare-hare kan ‘yan bindiga da sauran masu aikata miyagun laifuka.