✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

‘Yan sanda na neman Dino Melaye ruwa a jallo

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta sanar da cewa tana neman sanata Dino Melaye ruwa a jallo. Sanarwar ta nuna cewa ana neman sanatan ne da…

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta sanar da cewa tana neman sanata Dino Melaye ruwa a jallo.

Sanarwar ta nuna cewa ana neman sanatan ne da dan tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Abubakar Audu mai suna Mohammed Audu.

Rundunar ta ‘yan sanda ta ce tana neman mutanen guda biyu bisa zargin ba ‘yan sanda labarin karya, inda Dino ya yi zargin cewa an kai masa hari da nufin kashe shi bara.