✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan fashi 24 sun shiga hannu a Legas

Kwamishinan ya ce za a gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kotu.

An kama wasu mutum 24 da ake zargi da aikata fashi da makami da wasu laifuka a yankin Oshodi da ke Jihar Legas.

Kwamishinan Muhalli da Albarkatun Ruwa, Tokunbo Wahab ne, ya bayyana hakan a shafinsa na X.

Ya ce, “An kama wasu ‘yan fashi 24 a Oshodi jiya, kuma za a gurfanar da su a gaban kuliya domin yanke musu hukunci.”

A gefe guda kuma Kwamishinan, ya bayyana cewa jami’an Sashen Kula da Magudanar Ruwa daga Ma’aikatar Muhalli da Ruwa ta Jihar Legas, sun fara rushe wasu gine-ginen da aka yi a kan magudanar ruwa a yankin Ajiran da ke ƙaramar hukumar Eti-Osa.

Kwamishinan ya ce matakin na daga cikin yunkurin gwamnatin jihar, na dakile ambaliyar ruwa.

Ko a makon da ya gabata, sai da aka samu ambaliyar ruwa wadda ta yi sanadin lalacewar dukiyoyi masu tarin yawa, sakamakon mamakon ruwan sama da aka yi a jihar.