✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda biyu a Anambra

’Yan bindiga sun harbe ’yan sanda biyu har lahira a yankin Nnewi

’Yan bindiga sun harbe ’yan sanda biyu har lahira a yankin Nnewi da ke Jihar Anambra.

Maharan sun hallaka ’yan sanadin ne ta hanyar buɗe musu wuta tare da jefa abin fashewa a cikin motarsu ne.

’Yan sandan sun gamu da ajalinsu ne a yayin da suke gudunar da wani bincike a yankin, a cewar kakakin ’yan sandan jihar, Tochukwu Ikenga.

Ya bayyana cewa jami’an tsaro sun fara farautar maharan domin kamo su da tabbatar da sun girbi sakamakon wannan aika-aika.

Ya kuma buƙaci jama’a da su taimaka wa rundunar da bayanai da za su taimaka domin kamo bata-garin.