Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa (NCDC) ta sanar da karin mutum biyu da suka kamu da cutar Coronavirus a safiyar yau Laraba, hakan ya sa aka samu adadin mutane 46 da suka kamu da cutar.
An samu karin mutanen biyu ne a jihohin Legas da Osun.
Hukumar NCDC ta fitar da sanarwar ne da misalin karfe 07:00 na safiyar Laraba, inda suka tabbatar da mutum 46 suka kamu da cutar, biyu da suka kamu da cutar sun warke daya kuma ya rasu.