✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Tinubu ya sake tura malaman addinin Musulunci Nijar

Ya dauki matakin ne a matsayinsa na Shugaban ECOWAS

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya sake tura malaman addinin Musulunci zuwa Jamhuriyar Nijar domin sake tattaunawa da sojojin da suka yi juyin mulki.

Ya dauki matakin ne ranar Alhamis bayan ya gana da malaman karkashin jagorancin Sheikh Dahiru Usman Bauchi.

A kwanakin baya dai malaman sun je Yamai, babban birnin Nijar, inda suka samu tattaunawa da shugaban mulkin sojin kasar, Janar Abdulrahmane Tchiani.

Tinubu dai ya sanar da daukar matakin ne a matsayinsa na Shugaban Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Afirka ta Yamma (ECOWAS).

Tun bayan da sojojin suka kwace mulki daga hannun Mohammed Bazoum a ranar 26 ga watan Yuli, ECOWAS ta kakaba wa kasar jerin takunkumai, tare da barazanar daukar matakin soji.

Tuni dai kungiyar ta ba dakarunta umarnin kasancewa cikin shirin ko-ta-kwana a kokarin dawo da mulkin farar hula, duk da dai ba ta rufe kofar sulhu ba.