Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya karɓi baƙuncin Shugaban Senegal, Bassirou Diomaye Faye a fadar Aso Rock da ke Abuja.
Wannan shi karo na farko da shugaban mafi ƙarancin shekaru a nahiyyar Afirka ya kawo ziyara Nijeriya tun bayan zamansa Shugaban Senegal a watan Afrilun da ya gabata.
- Ƙarin ɗalibai 7 na Jami’ar Kogi 7 sun shaƙi iskar ’yanci
- Auren Marayu: Limamai sun yi wa Ministar Tinubu wankin babban bargo
Bayanai sun ce Bassirou Diomaye Faye mai shekaru 44 ya zo ziyarar aiki ne a Najeriya.
Sai dai zuwa babu masaniya a kan aikin da ya kawo Shugaban Senegal ɗin Najeriya.
![](https://i0.wp.com/aminiya.ng/wp-content/uploads/2024/05/20240516_193145.jpg?resize=640%2C427&ssl=1)
A watan Afrilu da ya gabata ne aka rantsar Bassirou Diomaye Faye a matsayin shugaban Senegal.
An rantsar da ɗan jam’iyyar adawar bayan ya ni nasara da kashi 54 cikin ɗari na kuri’un da aka kaɗa a zaben a kan abokin hamayyarsa na hadakar jam’iyyu masu mulki.
![](https://i0.wp.com/aminiya.ng/wp-content/uploads/2024/05/20240516_193141.jpg?resize=640%2C427&ssl=1)
Tinubu, wanda shi ne shugaban kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka (ECOWAS), ya karɓi bakuncin Bassirou Faye tare da wasu ƙusoshin gwamnatin ƙasar.