✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Tambuwal ya kawo wa Atiku rumfar zabensa

Gwamnan jihar Sakkwato Aminu Waziri Tambuwal ya kawo akwatin mazabarsa ta Sakandaren ’Yan Mata da ke Tambuwal a zaben Shugaban kasa, da Majalisar Tarayya. Tambuwal…

Gwamnan jihar Sakkwato Aminu Waziri Tambuwal ya kawo akwatin mazabarsa ta Sakandaren ’Yan Mata da ke Tambuwal a zaben Shugaban kasa, da Majalisar Tarayya.

Tambuwal wanda shi ne Babban Daraktan Kwamitin Yakin Neman Zaben Atiku-Okowa ’yan takarar shugaban kasa da mataimaki a PDP, yana takarar Sanatan Sakkwato ta Kudu ne, kuma ya yi nasara a rumfarsa da kuri’a 252.

A zaben shugaban kasa, Atiku na PDP ya yi nasara da kuri’a 250, yayin da Tinubu na APC ya samu kuri’a 44.

Kazalika a bangaren kujerar majalisar wakilai, PDP ta yi nasara sa kuri’a 247 yayin da APC ta samu 45.

Idan za a iy tunawa, Tambuwal yanje daga neman takarar shugaban kasa a PDP ya mara wa Atiku baya, wanda a karshe ya yi nasara a zaben fid-da gwani.