✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sojoji sun kashe ’yan bindiga 100 a Arewa maso Yamma

’Yan bindiga da masu garkuwa da mutane sun dandana kudarsu a hunnun sojoji

A ci gaba da fatattakai bata gari a yankin Arewa maso Yamma, sojoji sun bindige ’ya binidga 100 tare da tsare wasu 148 tare da kwato mutum 107 a hannunsu.

Rundunar dakarun tsaro ta Operation Sahel Sanity a yankin ta ce ta kwace bindigogi 143 da harsasai 3,261 daga ’yan bindigar wadanda aka kama shida daga cikin masu yi musu fasakwaurin makamai.

Mukaddamin Kakakin Rundunar, Birgediya Benard Onyeuko, ya ce masu yi wa ’yan fashi daji leken asiri 20 da masu yi musu safarar abinci 32 sun shiga hannu.

A jawabinsa a Babban Sansanin Soji da ke Faskari, Jihar Katsina babban hafsan ya ce sojojin sun cafke mutum 13 da ke sayar da shanun sata a Jihar da masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba guda 315 dauke da harmtattun makamai a Jihar Zamfara.

Rundunar ta ce ta kwato shanu 3,884 da tumaki 1,627 daga hannun barayin daji a jihohin Katsina da Kebbi da Sokoto da kuma Zamafara.

Sun kuma tarwatsa sansanoni 81 na ‘yan fashin daji ciki har da maboyar hatsabinin dan fashin daji da ake kira Dangote a Jihar Katsina.

Ya ce dakarun suka dakile hare-hare ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane guda 128 a yankin.