✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sojoji sun kashe manyan Kwamandojin ISWAP 3 a Borno

Rundunar ta kashe kwamandojin ne a harin ta’addanci da ba a yi nasara ba a kan Mallam Fatori da ke karamar hukumar Abadam a Jihar…

Rundunar Operation Hadin Kai (OPHK) da ke samun goyon bayan sojojin sama Air Component sun kashe wasu manyan kwamandojin Kungiyar ISWAP guda uku.

Rundunar ta kashe kwamandojin ne a harin ta’addanci da ba a yi nasara ba a kan Mallam Fatori da ke karamar hukumar Abadam a Jihar Borno.

Wata majiya mai tushe daga jami’an rundunar ta OPHK ta tabbatar a ranar Alhamis din nan cewa, kwamandojin da aka bayyana sunayensu: Amir Abu Ali Weldone da Amir Ibunu da Amir Abu Waldume, na daga cikin wadanda aka kashe a harin da aka kwashe sa’o’i hudu ana yi a sansanin ‘yan gudun hijira da ke Mallam Fatori.

A cewar majiyoyin, kwamandojin da aka kashe sun taka rawar gani wajen gudanar da ayyukan Kungiyar ISWAP, inda ake kyautata zaton Abu Ali Wadume ne ke jagorantar ayyukan ta’addanci a yankin Kerenoa kusa da kan iyakar Najeriya da Nijar.

Majiyoyin sun tabbatar da cewa, ‘yan ta’addan sun kaddamar da harin hadin gwiwa ne daga yankin Kaniram da sanyin safiyar Laraba, inda suka afkawa sojoji.

Mayakan ISWAP sun yi amfani da manyan makaman yaki hade da jirage marasa matuki ciki har da makamin (AGLs), amma sun gamu da turjiya daga sojojin kasa na rundunar ta OPHK da goyan bayan manyan makaman yaki da suka hada da tankokin yaki da suka rika amfani da su babu kakkautawa.

Majiyar na cewar sojojin sun samu nasarar dakile harin bayan kazamin fadan da ya tilastawa maharan ja da baya cikin rudani a gaggauce.

Rahoton na cewar, akalla ‘yan tada kayar baya 12 ne aka tabbatar da mutuwarsu, tare da kwato bindigogin AK-47 guda bakwai, manyan bindigogi guda uku samfurin (GPMGs), da makaman roka guda biyu (RPGs), da wasu bama-bamai.

“Har yanzu ana ci gaba kididdige barnar da aka yi wa ‘yan ta’addan, amma an tabbatar da kashe wadannan manyan kwamandojin guda uku da aka ambata sunayensu wanda kuwa hakan babbar nasara ce tga kokarin da mayakan sojojin Najeriya ke samu akan ‘yan ta’addan.