✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sojoji sun ceto mutum 9 daga hannun ‘yan bindiga a Kaduna 

Sun kuma yi nasarar kwato shanu 90 da aka sace.

Dakarun rundunar ‘Operation Forest Sanity’ ta Sojin Kasa na Najeriya sun ceto wasu mutum tara da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a Jihar Kaduna.

Dakarun sun samu nasarar kubutar da mutanen ne yayin wani samame da suka maboyar ‘yan bindigar da ke garin Kaso a Karamar Hukumar Chikun ta jihar.

Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kaduna, Samuel Aruwan ya ce sojojin sun yi artabu da ‘yan bindigar ne a babban titin Tantatu, lamarin da ya sa suka tsere cikin dajin.

A sanarwar da ya fitar a ranar Litinin, Aruwan ya ce Sojojin sun yi bincike a sansanin tare da ceto mutum tara da suka yi garkuwa da su.

“Sojojin sun kuma kwato shanu 90 da ‘yan bindigar da suka gudu suka bari wadanda za a mika su ga Hukumar Kula da Kiwon Dabobbi ta Jihar Kaduna domin tantance su,” in ji shi.

Ya ce an gudanar da wani samamen sirri a tsaunin Bawa Rikasa, inda aka samu nasarar kwato babura hudu a hannun barayin daji.

Aruwan, ya ce mutum tara da aka ceto za a tantance su kafin a sake sada su da iyalansu.