✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Shugaban Zimbabwe ya koma gida saboda tsananin rikicin kasar

Shugaban Kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa ya katse ziyarar kasashen duniya  da yake yi, inda ya koma gida bayan kwanakin da aka yi ana zanga-zangar adawa…

Shugaban Kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa ya katse ziyarar kasashen duniya  da yake yi, inda ya koma gida bayan kwanakin da aka yi ana zanga-zangar adawa da gwamnati har aka hallaka akalla mutum 12.

An fara zanga-zangar ce a makon jiya bayan da Mnangagwa ya sanar da karin farashin man fetur da kashi 150.

Yayin da zanga-zangar ta yi kamari, Mataimakin Shugaban Kasar Constantino Chiwenga, wanda tsohon Kwamandan Sojin kasar ne ya kaddamar da wani mummunan farmaki, inda ya sa jami’an tsaro suka harbi masu zanga-zanga da kuma jawo mutane daga gidajensu ana dukansu, kamar yadda Muryar Amurka ta ruwaito kungiyoyin ’yan gwagwarmaya suna fada.