✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Shugaban NUC ya ajiye mukaminsa, zai koma koyarwa a BUK

Ya ce zai koma BUK ya ci gaba da koyarwa

Shugaban Hukumar Kula da Jami’o’i ta Kasa (NUC) Farfesa Abubakar Adamu Rasheed, ya ajiye mukaminsa da kasin kansa.

Ya bayyana hakan ne a wata hirarsa da jaridar Punch ranar, inda ya ce zai koma ya ci gaba da koyarwarsa a Jami’ar Bayero da ke Kano.

Aminiya ta rawaito cewa tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ne ya nada Rasheed a shekara ta 2015.

An nada shi ne lokacin da Adamu Adamu yake Ministan Ilimi.

Najeriya dai ta sami yawan jami’o’i masu zaman kansu fiye da koyaushe a tarihi lokacin da Rasheed yake shugabancin NUC.

Sai dai an fuskanci yawan yajin aikin malamai da sauran ma’aikatan jami’o’i fiye da kowanne lokaci.

Kafin nadin nasa dai a 2015, ya shugabanci Jami’ar ta Bayero da ke Kano.