✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Saudiyya ta yi shirin duban watan Sallah

An girke manyan na’urorin hangen nesa domin aikin duban watan Shawwal.

Saudiyya ta kammala shirin duban watan sallah a wannan Alhamis din.

Shirin na zuwa ne a daidai lokacin da al’ummar Musulmi suka dauki azumi na 29.

Wannan na kunshe ne cikin sanarwar da mahukunta Masallatan Harami na Makkah da Madina suka fitar a Twitter.

Shafin na Haramain Sharifain ya bayyana cewa daga yau Alhamis za a fara duban watan na Shawwal.

An girke manyan na’urorin hangen nesa domin aikin duban watan Shawwal.

Ana sa ran fara duba watan Shawwal ne a birnin Sudair da misalin karfe 06:09 na yamma, sai garin Tumair inda za a fara duba da 06:22 na dare.

A nan gida Najeriya ma, Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III, ya bukaci al’umma su fara duban jaririn watan Shawwal daga yau Alhamis 29 ga watan Ramadan.