✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sarkin Tikau a Yobe ya riga mu gidan gaskiya 

Za a rika tunawa da Mai Tikau bisa karamcinsa, da kaunar talakawa.

Allah Ya yi wa mai martaba Sarkin Tikau, Alhaji Muhammadu Abubakar Ibn Grema rasuwa a ranar Juma’a.

Rasuwar sarkin mai daraja ta ɗaya ta jefa al’ummar Sabon Garin Nangere da ke Karamar Hukumar Nangere cikin ruɗani kamar yadda wakilinmu ya ruwaito.

Wata majiya da ke kusa da fadar Tikau ta ce, Sarkin ya rasu ne a Asibitin Kwararru na garin Potiskum bayan ya yi fama da gajeruwar rashin lafiya.

Majiyar ta ce sai nan gaba kadan za a sanar da cikakkun bayanai game da jana’izar marigayi sarkin na Tikau.

“Za a rika tunawa da Mai Tikau bisa karamcinsa, da kaunar talakawa, da kuma gwarzon kare muhalli tare da kula da harkokin addini,” kamar yadda wani mai rike da sarautar gargajiya a masarautar, Honarabul Abdulrahman Nangere ya bayyana wa Aminiya.

Masarautar Tikau ita ce daya tilo a Jihar Yobe wadda ake alakanta ta da masarautar ’yan kabilar kare-kare duk da cewar masarautar ta Tikau ta kunshi har da kabilun Fulani, Ngizim da sauransu.