✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Rikicin Zamfara: ‘Yan sanda sun kama mutum 23 da makamai

Hukumar ‘yan sandan jihar Zamfara ta ce, ta kama mutum 23 dauke  da makamai wanda ake zarginsu da cewa, su ne suka tada rikici a…

Hukumar ‘yan sandan jihar Zamfara ta ce, ta kama mutum 23 dauke  da makamai wanda ake zarginsu da cewa, su ne suka tada rikici a karamar hukumar Tsafe lokacin da matasa suka fara zanga-zanga a garin.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Zamfara Mista Usman Belel ne ya bayyana wa manema labarai hakan a Gusau babban birnin jihar lokacin da kurar rikicin ta lafa.

Jami’an tsaron sun ce, sun kama matasan dauke da bindigogi lokacin da suke ta kona motoci da gineginen karamar hukumar.