✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

RFI ta dauki nauyin buga rigunan Kano Pillars a yarjejeniyar N100m

Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars da gidan rediyon Faransa RFI Hausa suka sanya hannu kan yarjejeniya ta Naira Miliyan 100. A karkashin yarjejeniyar da…

Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars da gidan rediyon Faransa RFI Hausa suka sanya hannu kan yarjejeniya ta Naira Miliyan 100.
A karkashin yarjejeniyar da aka kulla a yau alhamis, kungiyar za ta karbi tsabar kudi Naira miliyan 45m da kuma samar da rigunan kakar wasa ga dukkan ‘yan wasan.
 
Haka kuma RFI za ta horar da jami’an yada labaran kulob din tare da wallafa wasu labarai da suka shafi kungiyar.
Sabon Manajan Pillars Ahmed Musa da Sakataren kungiyar ne suka sanya hannu a takardar a madadin kungiyar, yayin da Shugaban Sashen Hausa na RFI Joseph Penney da Babban Editan Bashir Ibrahim Idris suka sanya hannu a madadin kungiyar.
 
“Wannan ne karon farko da RFI ta dauki nauyin daukar nauyin wani abu da ya shafi wasan kwallon kafa a tarihi.” inji Penney
 
Yarjejeniyar ta tsawon shekara guda ce kawai.