✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Pantami da Amaechi za su bayyana a gaban majalisa

Za su amsa tambayoyi kan karbar rancen Dala miliyan 500 da sauransu

Majalisar Wakilai ta gayyaci Ministan Fasahar Sadarwa Isa Ali Pantami da Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi su bayyana a gabanta domin amsa tambayoyi kan rancen Dala miliyan 500 na aiki jirgin kasa da sauransu a fadin Najeriya.

Majalisar ta kuma gayyaci Ministar Kudi Zainab Ahmed Darekta Janar na Ofishin Kula da Basuka (DMO) Patience Oniha su zo tare da su domin bayani a kan rancen daga bankin shige da fice na kasar China.

Shugaban Kwamitin Sulhu da Tsare-tsare na Majalisar, Ossai Nicholas a ranar Talata ya bukaci ministocin su hallara ranar 17 ga watan Agusta.

Ossai Nicholas ya bukaci dukkansu da a kawo dukkan takardun yarjejeniyar da aka kulla tsakanin Ma’aikatar Sufuri ta Tarayya da kamfanin CCECC na kasar China kan aikin jirgin kasa na Abuja-Kaduna, Lagos-Ibadan, Ibadan-Kaduna da kuma Kaduna-Kano.