✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Osimhen da Asisat Oshiola sun zama gwarazan ’yan wasan Afirka na 2023

Victor Osimhen ya zama dan Najeriya namiji na farko da ya lashe kambin a shekaru 24, yan Kanu Nwanko da ya lashe a 1999

Dan wasan gaban Super Eagles, Victor Osimhen ya lashe Kyautar Gwarzon Dan Wasn Afrika na 2023, wanda hakan ya daga darajarsa a jerin manyan ’yan wasa na duniya.

A bangaren mata kuwa, Asisat Oshiola ta Kungiyar Super Falcon ta Najeriya kuma mai taka leda a kungiyar Barcelona ce ta zama gwarzuwar ’yar wasan Afirka a bana.

Karon farko ke nan tun shekarar 1999 da wani dan wasa daga Najeriya ya lashe kyautar a bangaren maza, bayan Kanu Nwankwo shekaru 24 da suka gabata.

Osimhen wanda ke taka leda a Napoli ya doke Achraf Hakimi na kasar Morocco da Mohamed Salah na Masar wajen lashe kyautar ta gwarzon Afrika.

Bajintar da Osimhen ya yi a kakar wasa ta bara wajen taimakawa Napoli ta lashe gasar Serie A ta kasar Italiya, ya ba shi damar lashe kambun.

Dan wasan ya jefa wa Napoli kwallo 26 a gasar ta Italiya kuma ya zama dan  wanda da ya fi jefa kwallo a karshen kakar.

An gudanar da bikin karrama gwarzon dan wasan na Afrika ne a birnin Marakesh na Morocco.