✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mutum miliyan 283 ne suke kwana da yunwa a Afirka – Adesina

Adadin kusan ɗaya bisa uku ke nan na masu fama da yunwa a duniya

Shugaban Bankin Raya Kasashen Afirka (AfDB), Dokta Akinwunmi Adesina, ya ce akalla mutum miliyan 283 ne suke kwana da yunwa a nahiyar Afirka.

Ya bayyana hakan ne a yayin tattaunawa da bayar da kyaututtuka kan abinci na duniya na Norman Borlaug na 2023 da ke Des Moines a Jihar Iowa da ke kasar Amurka a ranar Juma’a.

Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, wanda shi ma yake halartar taron a wani bangare na bunkasa manufar Shugaban Kasa Bola Tinubu kan wadata kasa da abinci, ya gabatar da azuminsa a ranar Laraba.

Sai dai da yake gabatar da jawabinsa mai taken “Daga Dakar zuwa Moines”, Dokta Adesina ya ce sun ware Dalar Amurka biliyan ɗaya domin farfado da masana’antun sarrafa kayan gona a Jihohin Najeriya 24.

Ya ce za su gudanar da shirin ne da hadin gwiwar Bankin Raya Musulunci (IsDB) da Asusun Bunkasa Noma na Duniya (IFAD).

“Duk da ci gaban da aka samu a fannin aikin gona a Afirka, kusan mutum miliyan 283 har yanzu suna kwana da yunwa a Afirka.

“Wannan kusan kaso ɗaya ne cikin uku na yawan masu fama da yunwa miliyan 828 da ke fadin duniya,” in ji Adesina.