✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mutanen da aka kashe a Binuwai sun ƙaru zuwa 72

Adadin ya ƙaru ne bayan gano ƙarin gawarwaki 13 a ranar Litinin a ƙananan hukumomin  Ukum da Logo.

Adadin mutanen da suka mutu a hare-haren da aka kai a Jihar Binuwai ya ƙaru zuwa 72.

Adadin ya ƙaru ne bayan gano ƙarin gawarwaki 13 a ranar Litinin a ƙananan hukumomin  Ukum da Logo.Adadin ya ƙaru ne bayan gano ƙarin gawarwaki 13 a ranar Litinin a ƙananan hukumomin  Ukum da Logo.

Da farko a ranar Lahadi Gwamna Hyacinth Alia a yayin da yake jawabin Ista a wani coci, ya sanar a yayin cewa an gano gawarwaki 59.

Daga bisani aka gano ƙarin gawarwaki a cikin jejin yankunan da aka kai hare-haren.

Kakakin gwamnan jihar, Isaac Uzaan, ya bayyana cewa an gano ƙarin gawarwaki 12 a Ƙaramar Hukumar Uku sauran mutum ɗaya kuma a Logo.

Tsakanin daren ranar Alhamis da safiyar Juma’a ne kai hare-hare a ƙauyukan yankin Sankera wanda ya ƙunshi ƙananan hukumar Ukum, Logo, and Kastina-Ala.