A karo na biyu a ƙasa da wata ɗaya ’yan bindiga sun sake miƙa makamansu ga sojoji, a wani ƙoƙari na samar da zaman lafiya a Jihar Katsina.
Aminiya ta ruwaito yadda a ranar 19 ga watan Janairun 2025, ’yan bindiga suka miƙa makamansu da mutanen da ke hannunsu, a wani zaman sulhu da jami’an tsaro suka yi da su a yankin Ƙaramar Hukumar Batsari ta Jihar Katsina.
Sani samu rabuwar kai
A gefe guda kuma wasu kuma na zargin Gwamnatin Tarayya Nana hannu wajen yin sulhu da ’yan ta’addan ta bayan fage domin a sami zaman lafiya a Jihar.
Wani mazaunin yankin ya ce, “Ba a gayyace mu ba amma na je na ga abin da aka yi. Kimanin motoci takwas na APC da hiluxs ɗauke da sojoji da ’yan sanda da jami’an tsaron CWC da ’yan banga.
“Na ga ’yan bindigar sun miƙa wa sojoji bindigogi biyu ƙirar Machine Gun sun neman a basu damar shiga garuruwanmu da kasuwanninu ba tare da wani ƙaido ba.
Gwamna Radda ya jaddada matsayinsa
Ya ce “mun sha faɗa cewa babu ɗan bindigar da za mu je mu roƙe shi don a samu zaman lafiya. Amma idan su da kansu suka zo suka miƙa wuya za mu karɓe su,” in ji a yayin wani gangamin yaƙin nemba Batsari gabanin zaɓen ƙananan hukumomin jihar da za a gudanar ranar Asabar.