✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mawakin Hausa Nazir Ahmad ya angwance

A Lahadin da ta gabata ce, fitaccen mawaki Nazir M. Ahmad; wanda aka fi sani da Sarkin Waka ya angwance. Hakan shi ya kawo karshen…

Na biyu daga hagu, ango Nazir ne tare da abokansa, a ranar daurin aurensaA Lahadin da ta gabata ce, fitaccen mawaki Nazir M. Ahmad; wanda aka fi sani da Sarkin Waka ya angwance. Hakan shi ya kawo karshen rade-radin da jama’a suka jima suna yi na cewar zai auri fitacciyar jarumar fim din Hausa Hadiza Aliyu Gabon.
Kafin zuwan wannan rana, jama’a suna ta yada jita-jitar cewa mawakin zai auri Hadiza Gabon. Hakan ba zai rasa nasaba da yadda jama’a ke yawan ganin jarumar tare da mawakin ba. An dade ana yawan ganin su tare a lokuta daban-daban, musamman ma duk wani taro da shi mawakin zai gabatar ko zai je, akan yawaita ganin su tare.
Auren jarumin ya kawar da wannan jita-jita ta hanyar angwancewa tare da amaryarsa, Hadiza Isyaku Ahmad. An daura auren nasu ne a masallacin Murtala da misalin karfe sha daya da rabi na safiyar Lahadin da ta gabata.
Limamin masallacin Murtala, Sheikh Malam Kabiru dantaura ne ya jagoranci daurin auren a bisa sadakin Naira dubu arba’in. Wakilin ango, wanda kuma ya kasance yayansa, Misbahu M Ahmad ne ya mika sadakin.
Tun kafin ranar daurin auren, an gudanar da shagulgulan biki a wurare daban-daban da suka hada da otel din Royal Tropicana da kuma Country Mall, wadanda duk suke a birnin Kano.
Jim kadan da kammala shagalin, wakilinmu ya tuntubi ango, mawaki Nazir dangane da rade-radin da aka dade ana yi game soyayyarsa da Hadiza Aliyu Gabon. mawakin ya ce: “Babu wata soyayya tsakanina da ita sai dai akwai kyakykyawar alaka tsakaninm da ita. Hakan shi ne ya sa jama’a suke ganin kamar akwai soyayya a tsakaninmu da ita amma sam-sam ba haka ba ne.”    
Taron bikin ya sami halartar mawaka da dama tare da jaruman fim din Hausa, wadanda suka hada har da ita Hadiza Aliyu Gabon.