✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mawaki Hassan Wayam ya riga mu gidan gaskiya

A cikin shekarar 1956 aka haifi Alhaji Hassan Wayam a wani gari mai suna Gwadda.

Allah ya yiwa shahararran mawakin nan na Hausa, Alhaji Hassan Wayam mai wakar Kukuma Easy rasuwa a cikin daren jiya.

An yi jana’izarsa yau Asabar da misalin karfe 9:00 na safe a gigansa da ke layin Zomo a Unguwar Falladan da ke Karamar Hukumar Sabon Gari a Zariya.

Tarihi ya nuna cewa a cikin shekarar 1956 aka haifi Alhaji Hassan Wayam a wani gari mai suna Gwadda, wanda kuma ake kira Bakin Ruba, a kasar Maradun ta Jihar Zamfara.

Mahaifin sa, Malam Muhammadu Babarbare ne mai sana’ar sassaka yayin da a wasu lokutan ya rika yi wa Fulani kidan kotso jefi-jefi.

Bayan Hassan ya kara wayo, sai ya koma garin Mayanci da ke kusa da Gusau, ya zama yaron kanikawa.

Kasancewar Mayanci bariki ce sosai a wancan lokacin, ga karuwai da ‘yan caca da sauran ‘yan duniya, a nan ne sha’awar sa da kade-kade ta yi zurfi, musamman kidan kukuma.