✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Maniyyatan da za su je Hajji a jirgin farko sun yi hatsari

Motar maniyyatan ta yi hatsari ne a ranar Laraba a kan hanyarsu ta zuwa Abuja inda za su hau jirgin farko a ranar Alhamis.

Maniyyatan aikin Hajjin bana daga Jihar Nasarawa da ke shirin tafiya a jirgin farko sun yi hatsari.

Rahotanni sun nuna mutum hudu sun samu rauni bayan motar maniyyatan ta yi adungure da su ne a ranar Laraba a kan hanyarsu ta zuwa Abuja inda za su hau farko a ranar Alhamis.

Hatsarin da ya ritsa da bas mai daukar mutum 18 da suke ciki ne a yankin Kara da ke Karamar Hukumar Keffi a Jihar Nasarawa.