✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Makarantar Jama’atu Collage ta yaye dalibai 692 a Saminaka

Makarantar Nazarin Addinin Musulunci ta Jama’atu College  da ke garin Saminaka a Jihar Kaduna, ta yaye dalibai 692 a karshen makon  jiya. Da yake jawabi…

Makarantar Nazarin Addinin Musulunci ta Jama’atu College  da ke garin Saminaka a Jihar Kaduna, ta yaye dalibai 692 a karshen makon  jiya.

Da yake jawabi a wajen taron yaye daliban Mai taimaka wa Gwamnan Jihar Kaduna na kan Harkokin Makarantun Islamiyya Malam Isma’ila Mainasara Muhammad ya ce babban kudirin gwamnatin Jihar Kaduna, kan makarantun Islamiyya  shi ne su samu ci gaba irin na zamani.

Ya ce gwamnatin tana tsare- tsare don ganin makarantun Islamiyya da makarantun Allo sun shiga tsarin gwamnati a jihar, don ganin daliban  makarantun sun zama kamar daliban makarantun zamani, ta yadda su ma za su  rika samun aikin gwamnati.

Ya yi kira ga makarantun Islamiyya  da malaman makarantun  su ci gaba da koya wa yara tarbiyya da zaman lafiya, domin a ci gaba da samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar da kasa baki daya.

A jawabin daya daga cikin shugabanin  makarantar Malam Nuhu Liman Saminaka ya ce suna kokarin kammala ginin mazaunin wannan makaranta na dindindin.

Ya ce manyan ’yan siyasa da masu hali  na yankin sun taimaka wajen sayen filin gina makarantar kan Naira miliyan 2. Kuma  makarantar  ta yi kokari wajen kara sayen wasu filaye da ke kusa da filin da ake ginin makarantar tare da kokarin gina ajujuwa 3  da ofishin malamai.

Ya ce nan ba da dadewa ba makarantar za ta  koma mazauninta na dindindin.

Ya yi  kira ga iyayen yara su kokarta su sanya ’ya’yansu a makarantar domin su karanci addini da tarbiyya da za su taimaka wa rayuwarsu a nan duniya da Lahira.

Tun farko a jawabin Mataimakin Shugaban Makarantar Malam Abdullahi Shu’aibu Liman Saminaka ya ce a bana a bangaren babbar sakandare sun yaye dalibai 45, a karamar sakandare sun yaye dalibai 250,  sai bangare firamare sun yaye dalibai 397.

Ya yi  kira ga al’ummar  yankin da kasa baki daya su kula da addinin Musulunci  sosai, domin shi ne zaman lafiyar al’umma a duniya da Lahira.