Majalisar Dattawa ta bukaci a sanya wa filin jirgin sama na Ibadan sunan tsohon Gwamnan Jihar Oyo, Marigayi Sanata Abiola Ajimobi.
Zaman Majalisar na ranar Talata ya bukaci Gwamnatin Tarayya ta sauya sunan filin jirgin domin tunawa da Ajimobi wanda shi ne Mataimakin Shugaban Marasa Rinjayenta a shekarar 2003 zuwa 2007, a lokacin da ya wakilci mazabar Oyo ta Kudu.
Mika bukatar hakan ga gwamnatin tarayya ta biyo bayan kudurin da Sanata Abdulfatahi Buhari (APC, Oyo) ya gabatar a lokacin zaman majalisar, wadda ta samu goyon bayan takwarorinsa.
Zauren majalisar ya kuma yi shiru na minti daya domin juyayin rasuwar tsohon gawmnan na Oyo wanda ya rasu a narar 25 ga watan Yuni yana da shekara 70 a duniya sakamakon rashin lafiya.
Related