✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Leicester City ta raba gari da Brendan Rodgers

Rodgers ya jagoranci Liverpool da Celtic kafin ya koma Leicester City a Fabrairun 2019.

Leicester City ta sallami kocinta Brendan Rodgers bayan kulob din ya sha kashi a hannun Crystal Palace a ranar Asabar.

Wannan ne karo na biyar da ake lallasa kungiyar a wasanni shida da ta buga a Gasar Firimiya Ingila.

A wani sako da kulob din ya wallafa a shafinsa na intanet, ya bayyana cewa “Kungiyar Leicester City ta cimma matsaya da Brendan Rodgers, inda zai bar kulob din bayan ya shafe shekara hudu a matsayinsa na kocin kulob din.

“Brendan zai bar filin wasa na King Power a matsayin daya daga cikin wadanda suka fi samun nasara a tarihin kulob din, bayan ya kai mu ga nasarar daukar kofin da muka dade muna son dauka na FA Cup a 2021,” in ji Leicester City.

Haka kuma kulob din ya kara da cewa a cikin matakai mafi girma a gasar Firimiya da kulob din ya kai, Brendan ne ya kai kungiyar matakin har sau biyu da kuma zagayen kusa da na karshe da kulob din ya kai a karon farko a gasar zakarun Turai ta Europa League a 2022.

Rodgers dai ya jagoranci Liverpool da Celtic kafin ya koma Leicester City a Fabrairun 2019.

Shi ma mataimakin kocin Leicester City Chris Davies da kuma kocin da ke kula motsa jiki na kulob din Glen Driscoll duk za su bar Leicester City.