✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kotu ta soke zaben Sanatan APC a Kogi, ta ce ’yar takarar PDP ce ta lashe

Kotun ta ce Natasha ta PDP ce ta lashe zaben

Kotun sauraron kararrakin zaben ’yan majalisa a Jihar Kogi ta soke zaben kujerar Sanatan Kogi ta Tsakiya, Abubakar Ohere.

Kotun ta kuma ayyana Natasha Akpoti-Uduagan ta jam’iyyar PDP a matsayin wacce ta lashe zaben ranar 25 ga watan Fabrairun da ya gabata.

Da take yanke hukunci, kotun, karkashin jagorancin Mai Shari’a K.A. Orjiako, ya ce an kara adadin yawan kuri’un da Ohere ya samu a akwati mai lamba 9 da ke Karamar Hukumar Ajaokuta.

Ya kuma ce jami’in hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ya rage kuri’un da PDP ta samu a mazabar yayin tattara sakamakon.

Alkalin ya kuma ce da gangan an ki shigar da sakamakon jam’iyyar PDP a wasu akwatina guda uku na dai waccan Karamar Hukumar.

Kotun ta ce sakamakon da Natasha ta samu a wadancan akwatinan guda 9 sun kama 1,073 ne ba 77 din da aka shigar mata ba, inda ta ce an kara wa dan takarar APC kuri’u daga 1,031 zuwa 1,553.