✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Katsina ta zama cibiyar haɗin kan ƙabilun ƙasa a Arewa — Gwamna Radda

Wannan muhimmiyar nasara ce ga Jihar Katsina da al’ummar ƙabilun Yarbawa da ke zaune a Jihohin Arewacin ƙasa baki ɗaya.

Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umaru Radda ya tabbatar da naɗin Sarkin Yarbawan Funtuwa, Oba Alhaji Murtala Sani Adeleke a matsayin sabon Sarkin Yarbawan Jihohin Arewa 19 har da Abuja.

Mataimakin Gwamnan JIhar Katsina, Malam Faruk Lawal Jobe ne ya tabbatar da naɗin a madadin gwamnan a lokacin da yake karɓar baƙuncin tawagar Sarakunan Yarbawan Arewa da suka miƙa masa takardar amincewarsu ga zaɓen Alhaji Murtala Sani Adeleke a matsayin sabon Sarkin Yarbawan Arewa a fadar gwamnati da ke Katsina.

Gwamnan ya nuna matuƙar farin ciki da jinjina wa yadda aka gudanar da zaɓen shugabannin Majalisar Sarakunan Yarbawan na Arewa lami lafiya.

Ya ce, zaɓen wanda shi ne irin sa na farko a tarihin zaman ƙabilun Yarbawa a Arewacin ƙasar, ya nuna alamar ɗorewar haɗin kan al’ummomin ƙasa ne da ci gabansu.

Ya ce, “Wannan muhimmiyar nasara ce ga Jihar Katsina da al’ummar ƙabilun Yarbawa da ke zaune a Jihohin Arewacin ƙasa baki ɗaya.”

Da yake yi wa Aminiya ƙarin haske, Sarkin Yarbawan Jihar Kano, Oba Murtala Alimi Otisese, wanda aka zaɓa a matsayin mataimakin Sarkin Yarbawan Arewa kuma shugaba na shirye-shiryen bikin wankan sarauta, ya ce, “a ranar Lahadi mai zuwa 15 ga watan Fabrairu ne za mu gudanar da wannan biki a birnin Abuja, inda za a miƙa wa sabon Sarkin Yarbawan Arewa Oba Murtala Sani Adeleke da ’yan majalisarsa takardun shaida (Satifiket) domin tabbatar da naɗinsu a hukumance.”

Oba Murtala Alimi Otisese ya ce, “muna sa ran halartar wasu sarakunan Yarbawa da manyan mutane daga Jihohi 6 na Kudu maso Yamma da sauran shugabanni daga sassa daban-daban na ƙasa zuwa wajen bikin a Abuja.”