Tun bayan da hukumomin Saudiyyar suka sanar kimanin watanni hudu da suka gabata cewa za a sake bude gidajen sinima a kasar bayan kusan shekara 40 da rufe su, abubuwa sun gudana cikin gaggawa na tabbatar wannan alkawari.
Ranar 18 ga wannan wata na Afrilu, ita ce Saudiyyar ta sa domin bude kofar sinimar ta farko a babban birnin kasar, Riyadh.