✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kasar Saudiya za ta bude gidan sinima na farko

Kasar Saudiya ta bayar da sanarwar cewa za ta bude gidan sinimarta na farko tun shekarar 1970 da aka taba bude sinima a kasar, nan…

Kasar Saudiya ta bayar da sanarwar cewa za ta bude gidan sinimarta na farko tun shekarar 1970 da aka taba bude sinima a kasar, nan da mako biyu.

Bude wannan sinimar dai zai zamo na farko ne kafin sauran su biyo baya, inda ake sa ran za a bude kusan sinima 40 a fadin kasar nan da shekarar 2030, kamar yadda BBC ta ruwaito.

Tun bayan da hukumomin Saudiyyar suka sanar kimanin watanni hudu da suka gabata cewa za a sake bude gidajen sinima a kasar bayan kusan shekara 40 da rufe su, abubuwa sun gudana cikin gaggawa na tabbatar wannan alkawari.

Ranar 18 ga wannan wata na Afrilu, ita ce Saudiyyar ta sa domin bude kofar sinimar ta farko a babban birnin kasar, Riyadh.