✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Jamus za ta dawo da ’yan Najeriya 14,000 da ke kasarta gida

Jamus ta ce mutanen na zaune ne kara-zube a kasar

Shugaban gwamnatin Jamus, Olaf Scholz, ya ce akalla ’yan Najeriya 14,000 da ke zaune a kasarsa ne suke fuskantar barazanar a fitar da su daga kasar.

Ya ce za su dauki matakin ne saboda ƙaruwar yadda ’yan Najeriya ke neman mafaka a kasar ba tare da cikakkun takardun shaidar gane ko su su wane ne ba.

Olaf ya kuma ce akalla ’yan Najeriya 12,500 ne suke zaune kara-zube sakamakon gwamnatin Najeriyar tana barin wadanda ba su cika ka’ida ba su bar kasar.

Da yake jawabi yayin wata tattaunawa da Shugaban Kasa Bola Tuntubi a Abuja ranar Talata, Olaf ya ce, “Karuwar yawan ’yan Najeriyar da suke neman mafaka a Jamus a 2023 ya yi tashin gwauron zabo.

“Kusan mutum 14,000 ne za mu iya mayarwa kasarsu, kuma akasarinsu ma ba su da halastattun takardun zama a kasar.

“A shirye muke mu hada gwiwa domin inganta harkokin shige da fice a tsakaninmu,” kamar yadda wata sanarwa daga Fadar Shugaban ta fada.

A wani labarin kuma, Shugaba Tinubu ya ce akwai damar ci gaba da tattaunawa domin ganin ba a kai ga dawo da su gida ba.