✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Jakadan Saudiyya a Najeriya Adnan bin Mahmoud Bostaji ya rasu

Ofishin jakadancin Saudiyya a Najeriya ya bayar da sanarwar rasuwar jakadan kasar a Najeriya Adnan bin Mahmoud Bostaji a yau Talata. Majiyarmu ta samu rahoton…

Ofishin jakadancin Saudiyya a Najeriya ya bayar da sanarwar rasuwar jakadan kasar a Najeriya Adnan bin Mahmoud Bostaji a yau Talata.

Majiyarmu ta samu rahoton cewa, kwanan ne iyalan Jakadan suka koma Saudiyya inda shi kuma yake Najeriya.

Rahoton ya kara da cewa, a daren yau Talata za a tafi da marigayin kasar Saudiyya.

Jakadan ya soma aiki da ma’aikatar harkokin wajen Saudiyya a shekarar 1991, a wannan shekara ne kuma aka nada shi a matsayin jakadan Saudiyya a Tehran wato babban birnin Iran, inda ya ci gaba da aiki har zuwa 1998.

Sannan ya kuma taba zama wakili a majalisar hada kan kasashen Gabas Ta Tsakiya tun daga 1998 har zuwa 2000.