✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ina neman yafiyar magoya bayan Arsenal kan shan kaye a hannun Brighton —Arteta

Arteta ya ce abu ne mai yiwuwa Arsenal ta lashe Firimiyar Ingila ta bana.

Kociyan Arsenal, Mikel Arteta, ya nemi afuwar magoya baya dangane da shan kayen da kungiyar ta yi har gida a hannun Brighton da kwallaye 3 da nema a ranar Lahadi.

Rashin nasarar da Arsenal ta yi ya sa kungiyar ta barar da damarta ta karshe a rige-rigen lashe kofin Firimiyar Ingila tsakaninta da Manchester City.

Gunners dai ta shafe tsawon lokaci tana jagorancin teburin gasar ta Firimiya, a kokarin kawo karshen dakon shekaru 19 da ta yi a baya don kai kofin gida.

To sai dai Arsenal wadda ta lashe Kofin har sau 11 a tarihi, ta gamu da gagarumin matsin lamba a watannin baya-bayan nan daga City.

Wasanni 2 cikin 7 da Arsenal ta doka a baya-bayan nan kadai ta iya samun nasara, wanda ke nuna yiwuwar bankwananta da kofin na Firimiya daidai lokacin da ake da tazarar maki 4 tsakaninta da City, kuma tawagar ta Guardiola ke da wasa guda a hannu.

A jawabinsa gaban manema labarai Arteta ya ce salon wasan da Arsenal ta yi a zagaye na biyu na haduwar ta jiya sam ba abin karba ba ne.

A cewarsa a lissafe, iya lashe kofin na Firimiya ga Arsenal har yanzu abu ne mai yiwuwa amma a yanzu abin da ya fi muhimmanci garesu shi ne samar da gyara ga kura-kuren da suka yi a jiya.

Idan har Arsenal ta gaza nasara a haduwarta da Nottingham Forest a lahadi mai zuwa, kuma City ta yi nasara kan Chelsea a ranar 21 ga watan nan, kai tsaye tawagar ta Pep Guardiola ta lashe kofin karo na 5 cikin shekaru shida.