✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ighalo ya lashe gwarzon dan kwallon Afirka na Ingila

dan kwallon kulob din Watford na Ingila kuma haifaffen Najeriya Odion Igahlo ne aka zaba a matsayin Gwarzon dan kwallon Afirka da ke buga kwallo…

dan kwallon kulob din Watford na Ingila kuma haifaffen Najeriya Odion Igahlo ne aka zaba a matsayin Gwarzon dan kwallon Afirka da ke buga kwallo a gasar rukunin firimiya ta Ingila.
Gasar wacce ake gudanar da ita a tsakanin ’yan kwallon da suka fito daga Nahiyar Afirka amma suke wasa a gasar rukunin firimiya, ana yin ta ne a duk karshen wata.  Wata cibiya da ke kula da yadda ake tafiyar da harkokin kwallon kafa mai suna New African Soccer ce take gudanar da gasar.
A wata sanarwa da cibiyar ta fitar wacce ta samu sanya hannu Daraktanta Tunde Adelakan ta ce “ Abin da ya sa aka zabi Ighalo ba tare da hamayya ba shi ne ganin yadda ya shafe daukacin watan Disamban 2015 yana zura kwallo a wasanni shida da ya buga wa kulob din Watford a gasar firimiya.  Hasalima dan kwallon ya samu nasarar zura kwallaye a ragar Chlesea da Liberpool da Tottenham a wasannin firimiyar da ya gudana a Ingila a watan Disambar 2015.  Hakan ce ta sa aka zabi dan kwallon a matsayin Gwarzon dan kwallon firimiya na watan Disamban 2015 ba tare da hamayya ba”.
Tunde Adelakan ya ce a tsawon lokacin da aka yi ana gudanar da wannan gasa, Ighalo ne ya kasance na farko da ya lashe kyautar har sau biyu.  Ya taba lashe gasar a watan Oktoban 2015 kafin yanzu da ya sake lashe wa a watan Disamban 2015.
Ighalo dai ya zura kwallaye 14 daga cikin wasanni 20 da ya yi wa kulob din Watford a gasar firimiya.  Kawo yanzu shi ne dan kwallo na uku a jerin sunayen ’yan kwallon da suka fi zura kwallo a raga a gasar.