Wasu magidanta ‘yan uwan juna da Allah ya jarabta da makanta sun bayyana cewa bara kaskanci ne don haka suka rike sana’ar nika garin albo.…
‘Yan uwa uku magidanta masu lalurar makanta da ke sana’ar nikan garin albo
DagaAbbas Dalibi
Wed, 7 Oct 2020 9:45:35 GMT+0100
Wasu magidanta ‘yan uwan juna da Allah ya jarabta da makanta sun bayyana cewa bara kaskanci ne don haka suka rike sana’ar nika garin albo.
Magidantan uku, masu shekaru daga 60 zuwa 54 mazauna garin Ago-Aare, Jihar Oyo, sun shaida wa Aminiya cewa cutar makantar ta same su ne a lokacin da suke cika shekaru 30 a rayuwarsu.
Babban su mai suna Muhammadu Sa’adu Isiyaka ya ce kaninsa Sulaiman Isiyaka wanda ke sana’ar dabbobi, shi ne ya sayi injin nika garin alabo wanda yanzu suke amfani da shi a sana’ar da suke dogaro da ita.
Aminiya ta dauko muku hotunan makafin uku da yadda suke sana’ar su ta mika garin albo.
Nasiru Isiyaka da dan uwansa Sa’adu Isiyaka a lokacin da suke kokarin tayar da injin nikan alabo
Nasiru isiyaka yana kokarin tayar da injin nika.
Sa’adu isiyaka yana kokarin sanya bel bayan da dan uwansa ya tada injin nikan
Nasiru Isiyaka yana zuba busasshiyar doyar da ake nikawa ta koma garin albo da ake yin amala da ita
Sa’adu Isiyaka, makaho mai shekara 60, ya ce cutar makanta ta kama shi yana da shekara 30 a duniya, kuma bai taba yin bara ba sai ya kama sana’ar nikan garin albo bayan da kaninsa Sulaiman wanda shi ma makaho ne da ke sana’ar sayar da dabobbi ya saya injin nika
Nasiru Isiyaka, makaho da ke nikan albo
‘Yan uwa uku magidanta masu lalurar makanta da ke sana’ar nikan garin albo
Shagon da makafin ke amfani da shi na nika garin albo