Tawagar kwallon kafa ta Holland ba ta gayyaci Memphis Depay da Robin ban Persie ba a cikin ‘yan kwallon da za su buga mata wasan sada zumunta da Wales.
Wales ce za ta karbi bakuncin Netherlands a wasan sada zumunta da za su fafata a filin wasa na Cardiff a ranar 13 ga wannan wata da muke ciki.
Depay mai taka leda a kulob din Manchester United da ke Ingila kawo yanzu ya zura kwallaye 19 a kulob din Manchester da kuma a kungiyar kwallon kafa ta Holland. Shi kuma Robin ban Persie da ke kwallo a kulob din Fenerbahce na Turkiyya kawo yanzu ya zura kwallaye biyar a raga daga wasanni 16 da ya yi a bana.
Sai dai kuma Netherlands din wacce ta kasa samun gurbin shiga gasar cin kofin Nahiyar Turai (Euro) da za a yi a Faransa a badi, ta gayyato Arjen Robben dan kwallon Bayern Munich da ke Jamus wanda ya warke daga jinya.
Wales ta samu tikitin shiga gasar cin kofin Nahiyar Turai da za a yi a 2016, kuma rabon da ta halarci babbar gasar kwallon kafa tun a kofin duniya da ta buga a shekarar 1958.