Gola kuma Mataimakin Kyaftin din kungiyar Super Eagles na Najeriya bincent Enyeama, ya ce har yanzu akwai burin da yake so ya cim ma a Super Eagles.
Enyeama mai kimanin shekara 31 wanda Hukumar kwallon kafa ta Duniya (FIFA) ta zaba a matsayin Gwarzon Gola na Afirka, ya bayyana hakan ne, sakamakon jita-jitar da ake yadawa cewa ya yi ritayar buga wa Najeriya wasa.
Ya karyata jita-jitar ne a lokacin da ya yi wata hira da shafin intanet na gidan Talabijin din Super Sport a ranar Lahadi.
“Ban ce na daina buga wa Najeriya wasa ba, na ce zan y i shawara da iyalina da kuma abokaina. Amma har yanzu akwai burin da nake so na cim ma a Super Eagles.”
Har yanzu akwai burin da nake so in cim ma a Super Eagles – Enyeama
Gola kuma Mataimakin Kyaftin din kungiyar Super Eagles na Najeriya bincent Enyeama, ya ce har yanzu akwai burin da yake so ya cim ma a…