✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Hajji: Gwamnatin Katsina ta biya wa maniyyata 2000 kuɗin hadaya

A shekarar da gabata ma gwamnatin jihar ta biya wa mahajjatan jihar kuɗin hadaya.

Gwamnatin Jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Gwamna Malam Dikko Umar Radda, ta biya wa maniyyatan jihar 2,047 kuɗin hadaya domin sauƙaƙa musu wajen hidimomin aikin Hajji na shekarar 2025.

Amirul Hajji kuma Mataimakin gwamnan jihar, Malam Faruk Lawal Jobe, ne ya bayyana haka a ranar Lahadi yayin da yake yi wa mahajjatan jirgin farko bankwana kafin tashin zuwa ƙasa mai tsarki.

Ya ce an biya wa kowane maniyyaci Riyal 600.

Mahajjatan da za su fara tafiya sun fito ne daga ƙananan hukumomin kudancin jihar, kuma za su tashi a jirgin kamfanin Max Air.

Gwamna Radda ya ja hankalin maniyyata da su kiyaye dokoki da ƙa’idojin aikin Hajji.

Haka kuma ya roƙe su da su yi addu’a don samun zaman lafiya da ci gaban Jihar Katsina da ma Najeriya baki ɗaya.

A shekarar da ta gabata ma, Gwamna Radda ya biya wa mahajjatan jihar kuɗin hadaya domin rage musu kashe kuɗi a aikin Hajji.