✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gwamnatin Najeriya na zargin Peter Obi da cin amanar kasa

Gwamnatin ta ce Obi ba dan Dimokuradiyyar da yake ikirari ba ne

Gwamnatin Tarayya ta shawarci dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar LP a zaben da ya gabata, Peter Obi, da ya guji tunzura jama’a su tayar da zaune tsaye kan sakamakon zaben da ya gabata.

Ministan Yada Labarai da Al’adu, Alhaji Lai Mohammed ne ya bayar da shawarar yayin wata tattaunawarsa da kafafen yada labarai a birnin Washington DC na Amurka.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa Ministan ya je Amurka ne don tattaunawa da kafofin kan abubuwan da suka wakana yayin zaben da ya gabata a Najeriya.

NAN ya ce ya zuwa yanzu, Ministan ya tattauna da jaridar Washington Post da Muryar Amurka da mujallar Foreign Policy da kuma kamfanin dillancin labarai na AP.

Lai Mohammed ya kuma gargadi Peter Obi da cewa ba daidai ba ne ya rika neman hakkinsa a kotu, sannan kuma ya rika kokarin tayar da zaune tsaye a daya bangaren.

“Obi da Mataimakinsa Datti, bai kamata su rika yi wa zababben Shugaban Najeriya, Bola Tinubu na APC barazana cewa muddin aka rantsar da shi ranar 29 ga watan Mayu mai zuwa, Dimokuradiyya ta kare a Najeriya.

“Wannan cin amanar kasa ne. Neman tayar da zaune tsaye ne. Kuma abin da suke kokarin yi ke nan.

“Kalaman Obi dan ko a mutu ko a yi rai ne, bai mai son Dimokuradiyyar da yake ikirari ba ne shi, saboda mai sonta bai kamata ya yi amanna da ita kawai lokacin da ya lashe zabe ba,” in ji Ministan.

Lai Mohammed ya kuma ce da Peter Obi da Atiku Abubakar na PDP sam ba su lashe zaben Shugaban Kasa ba saboda ba su cika ka’idojin da doka ta tanada ba.