Gwamnatin jihar Kano ta yi alkawarin kafa kwamitin dakarun lura da magunguna don taimakawa Hukumar Yaki da Muggan Kwayoyi ta NDLEA yaki da muggan kwayoyi a jihar.
Shugaban Hukumar Karbar Korafi da Yaki da Cin Hanci da Rashawa, Muhuyi Magaji Rimin-Gado, shi ne ya bayyana haka yayin da ya karbi tawagar Kwamandan Hukumar NDLEA na jihar, Hamza Umar a ofishinsa.
Rimin-Gado ya ce dakarun za su yi aiki tare da jami’an Hukumar NDLEA su yaki ta’ammuli da muggan kwayoyi a tsakanin matasan jihar.
Ya ce gwamnati ta dauki matakin don tallafa wa kokarin gwamnatin tarayya na yaki ga muggan kwayoyi a kasa baki daya.